Amurka ta tura wani karamin rukuni na dakarunta zuwa Najeriya, a cewar babban janar din da ke kula da rundunar sojin Amurka a Afirka, a ranar Talata.
Wannan shi ne karo na farko da Amurka ta amince a fili cewa tana da sojoji a kasa a Najeriya tun bayan kai hari kasar a ranar Kirsimeti.
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayar da umarnin kai harin ne a watan Disamba kan wuraren da ya bayyana a matsayin sansanonin kungiyar ‘yan ta’adan IS a Najeriya, inda ya ce ana iya ci gaba da daukar matakan soja nan gaba.