Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa a Najeriya INEC, ta ayyana ranar 20 ga watan Fabrairu a matsayin ranar zaben shugaban kasa na 2027.
Shugaban hukumar Farfesa Joash Amupitan ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a Abuja, inda ya kara da cewa, su ma zabukan ‘yan majalisun tarayya za’a gudanar da su ne a ranar da za’a yi na shugaban kasa.
Sannan za’a gudanar da na zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi kuma a ranar 6 ga watan Maris din shekarar 2027.
Shugaban hukumar zaben ya ce, shirye shirye sun kammala wajen tunkarar babban zaben na shekarar 2027.