Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Majalisar jihar Ribas ta dakatar da zaman tsige Fubara

Majalisar Dokokin Jihar Ribas ta dakatar da zaman tsige gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyyarsa, Ngozi Odu, bayan shiga tsakani da shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu ya yi.

Majalisar ta gabatar da kudirin dakatar da zaman tsigewan a yau Alhamis.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa a zamanta na farko a shekarar 2026, majalisar ta fara zaman tsige Fubara da mataimakiyyarsa bisa zargin aikata manyan laifuka, ciki har da rushe ginin majalisar jihar da kashe kudi ba tare da amincewar majalisar ba.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use