Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

‘Yan sanda sun tabbatar da mutuwar yara biyar sanadiyar gubar abinci

Rundunar ‘yan sandan jihar Taraba ta tabbatar da mutuwar yara biyar sakamakon zargin gubar abinci a garin Takum, yayin da wasu takwas ke kwance a asibiti.

Kakakin rundunar, ASP Victor Mshelizah, ya ce yaran sun ci naman da ake zargin ya lalace a yayin wani karatun Ramadan.
Tuni aka fara bincike domin gano musabbabin lamarin.

Wani lauyan kare hakkin bil’adama a Jalingo, Barrista Bilyaminu Maihanci, ya bukaci gwamnati da hukumomin da abin ya shafa su gudanar da sahihin bincike domin tabbatar da adalci ga iyalan wadanda suka rasu.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use