Hukumar karɓar Ƙorafe-ƙorafe da yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta fara kwato motocin gwamnati daga hannun wasu tsofaffin jami’ai da ake zargin sun ƙi mayar da su bayan kammala wa’adin aikinsu.
Shugaban hukumar, Sa’idu Yahaya, ya ce tun farko an aika musu da wasiƙun neman su mayar da motocin, amma wasu ba su bi umarnin ba, wanda ya sa aka ɗauki matakin kwato su domin kare dukiyar al’umma.
Daga cikin waɗanda aka kwato motocin a hannunsu akwai tsofaffin kwamishinoni da dama. Hukumar ta jaddada aniyarta ta ci gaba da kare kadarorin gwamnati da tabbatar da gaskiya da riƙon amana a jihar Kano.