Rundunar sojin Isra’ila ta IDF ta sanar da mutuwar dakarunta biyu a yayin wani faɗa a kudancin Lebanon.
Rundunar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Telegram, inda ta bayyana sunan ɗaya daga cikin sojojin da suka mutu a matsayin Maher Khatar, ɗan shekara 38.
IDF ta bayyana cewa Khatar yana aiki ne a cikin sashen faɗa na rundunar sojin Isra’ila, inda aka ce ya rasa ransa yayin artabu da mayaƙa a yankin da ake fama da tashin hankali.
Haka kuma rundunar ta tabbatar da cewa wani sojan Isra’ila na biyu ma ya mutu a wannan farmaki, sai dai har yanzu ba a bayyana cikakkun bayanansa ba a hukumance.
Sojojin Isra’ila sun ce tuni sun sanar da iyalan sojan na biyu game da mutuwar tasa, kuma za a bayyana sunansa ne bayan an kammala sanar da dangi da kuma sauran matakan da suka dace.
Rikici tsakanin sojojin Isra’ila da mayaƙan Hezbollah a kudancin Lebanon ya ƙara tsananta a ‘yan kwanakin nan, inda ake ci gaba da musayar wuta a yankin iyakar kasashen biyu.