Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya ce akwai yiwuwar a kai harin ta’addanci kan ofishin jakadancinta da makarantunta da ke kasar.
Ofishin jakadancin ya shawarci ‘yan ƙasar su riƙa sauya hanyoyi da lokutan tafiye-tafiye da kuma kauce wa tafiyar da rayuwarsu ta yadda za a iya hasashen abin da za su yi nan gaba tare da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana.
Wannan gargadi na zuwa ne yayin da yaƙi tsakanin Amurka-Isra’ila da Iran ke ci gaba da tsananta cikin kasa da mako biyu da fara yakin.
Sauran shawarwarin da Amurkar ta bai wa ‘yan kasarta a Najeriya sun haɗa da tabbatar da cewa wayoyin salularsu na da cikakken caji domin ko-ta-kwana da kuma sanin hanyoyin ficewa cikin gaggawa kafin su shiga ko wane gini.
Sai dai hukumomi sun ce duk da haka ofisoshin jakadancin za su ci gaba da aiki.