Sojojin Isra’ila sun ce sun gano cewa akwai jerin makamai masu linzami na Iran da ke shirin kai hari zuwa kasar.
A cikin wata sanarwa, sun ce tsarin tsaron kasar na aiki don “kawar da barazanar” kuma ana aika sanarwar wayar hannu ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
Kamfanin dillancin labarai na Tasnim na Iran ya kuma bayar da rahoton cewa an harba makami mai linzami zuwa Isra’ila.