Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Senegal ta bukaci a yi bincike kan gasar AFCON 2025

Shugaban Senegal Bassirou Doumaye Faye

Gwamnatin ƙasar Senegal ta buƙaci a gudanar da bincike kan hukuncin da aka yanke na ƙwace musu kofin gasar AFCON 2025.

Wannan ya biyo matakin da Hukumar CAF ta ɗauka na sauya sakamakon wasan ƙarshe tare da bai wa Morocco nasara.

Senegal ta bayyana hukuncin a matsayin rashin adalci, tare da zargin cewa an yi kuskure a yadda aka tafiyar da lamarin.

Haka kuma, ta ce za ta ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Sulhu ta Wasanni (CAS) domin neman a sake duba hukuncin.

Lamarin ya jawo cece-kuce a fannin ƙwallon ƙafa a Afirka, yayin da ake jiran sakamakon matakan da Senegal za ta ɗauka.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use