Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

ADC ta soki shugaba Tinubu kan taɓarɓarewar tsaro a Najeriya

Kakakin Jam'iyyar ADC na ƙasa, Bolaji Abdullahi Kakakin Jam'iyyar ADC na ƙasa, Bolaji Abdullahi
Kakakin Jam'iyyar ADC na ƙasa, Bolaji Abdullahi

Jam’iyyar hadaka ta ADC ta soki gwamnatin Bola Tinubu kan yadda Najeriya ta samu koma baya a rahoton matsayin tsaro na duniya na (Global Terrorism Index).

Jam’iyyar ta bayyana hakan a matsayin gazawa wajen kare rayukan ‘yan ƙasa da tabbatar da tsaro.

A wata sanarwa da Bolaji Abdullahi, Sakataren yada labarai na jam’iyyar, ya fitar, ADC ta ce rahoton na 2026 ya nuna cewa Najeriya ta tashi zuwa matsayi na huɗu a jerin kasashen da tashe‑tashen hankula da ta’addanci ya yi galaba akansu a duniya.


Rahoton ya bayyana samu mutuwar mutane 750 a shekarar 2025, karin kaso 46% idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

Jam’iyyar ta jaddada cewa wannan rahoto ba kawai lissafi ne ba, amma shaida ce ta raunana tsarin tsaro a ƙasar, inda hare‑haren ta’adda suka ƙaru, musamman a Borno State, inda fararen hula ke fi samun hasara.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use