Kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito cewa Amurka da Isra’ila sun kai hari cibiyar nukiliya ta Natanz a safiyar yau.
Rahoton ya bayyana cewa harin ya shafi wani ɓangare na cibiyar da ke da muhimmanci wajen shirin nukiliyar Iran, lamarin da ya ƙara tayar da hankali a yankin.
Sai dai kamfanin ya tabbatar da cewa ba a samu yoyo ko zubar sinadarin radiation sakamakon harin ba.
Haka kuma, an ce babu wata barazana ga mazauna yankunan da ke kewaye da cibiyar duk da harin da aka kai.