Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Trump ya ce Amurka na tunanin kawo ƙarshen hare-haren soja kan Iran

Shugaban Amurka, Donald Trump

Shugaba Donald Trump ya bayyana cewa Amurka na duba yiwuwar kawo karshen hare-haren soja da take kai wa ƙasar Iran, inda ya ce ƙasashen duniya da ke amfani da Mashigar Hormuz su su sanya ido tare da kula da ita.

A cikin wani saƙon da ya wallafa a shafin sada zumunta na Truth, Trump ya ce “mun kusa cim ma muradunmu, don haka muna duba yiwuwar kawo ƙarshen ayyukan sojojinmu a Gabas ta Tsakiya kan gwamnatin ta’addanci ta Iran.”

Ya ƙara da cewa ya kamata ƙasashen da ke amfani da Mashigar Hormuz su kula da ita da sanya ido a kanta, yanamai cewa “Amurka ba za ta yi hakan ba.”

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use