Fitaccen malamin addini a jihar Kaduna, Sheikh Ahmad Tijjani Umar ya yi watsi da batun kama shi da ake ta yaya ta wa.
Hakan na zuwa ne bayan kalaman tsohon dan takarar shugaban kasa a jama’iyyar Labour, Peter Obi, ya yi na cewa hukumar DSS ta cafke malamin a safiyar yau Talata, kan gayyatar da malamin ya yi masa zuwa gidansa da ke jihar Kaduna a ranar Lahadi.
Sheikh Ahmad Tijjani ya ce babu wani jami’in DSS da ya kama shi ko ya tuhumeshi kan zuwan Obi gidansa.