Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Matsalar tsaro ta kara ta’azzara fiye da kima a mulkin Tinubu – Baba-Ahmed

Tsohon mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin siyasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya ce Najeriya na cikin matsala mai tsanani fiye da lokacin da shugaba Tinubu ya karɓi mulki a 2023, yana mai danganta hakan da ƙaruwar matsalar tsaro da na rayuwa.

Baba-Ahmed ya bayyana cewa bayan kusan shekaru uku na mulkin Tinubu, hare-haren ta’addanci da tasirinsu sun ƙaru sosai, inda ya ce irin wannan yanayi bai taba kai wannan mataki ba a baya.

Ya yi wannan bayani ne a wata hira da ya yi da manema labarai, inda ya jaddada cewa gwamnati ta gaza cika alkawurran da ta ɗauka na kawo ƙarshen rashin tsaro da inganta rayuwar al’umma.

A cewarsa, Tinubu ya hau mulki ne da alkawarin samar da tsaro da walwala ga ‘yan Najeriya, amma har yanzu mutane na fuskantar matsaloli masu tsanani, musamman a fannin tsaro da tattalin arziki.

Baba-Ahmed ya kuma soki ziyarar da shugaban ya kai Birtaniya kwanan nan, inda ya ce ta zo ne a lokacin da ake fuskantar munanan hare-hare a cikin ƙasar – ya yi kira ga gwamnati da ta ɗauki matakan gaggawa don shawo kan matsalolin da ke ƙara ta’azzara.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use