Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Dalilin da ya sa Tinubu ya yi ta’aziyya a filin jirgi — Fadar shugaban ƙasa

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce dalilin da ya sa Bola Ahmed Tinubu ya gana da waɗanda harin Filato ya shafa a filin jirgin saman Jos shi ne rashin samun damar saukan jiragen sama da dare a filin jirgin.

Ta bayyana cewa wannan matsala ce ta lantarki, wanda ya sa aka zaɓi a yi ganawar a kusa da filin jirgi domin kauce wa matsalar tafiya cikin dare.

Lamarin dai ya biyo bayan hare-haren da suka yi sanadin mutuwar mutane da dama a jihar Filato, yayin da wasu ‘yan siyasa suka soki yadda aka gudanar da ziyarar a filin jirgi maimakon shigowa cikin gari domin ganewa idon sa halin da ake ciki.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use