Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske
Shugaban INEC ya wanke kansa daga zargin nuna fifiko a rikicin ADC
Ku dakatar da tarukan jam’iyya, ku dauki darasi daga Zamfara da Filato – INEC ta gargadi ADC
Iran ta harbo jirgin yaƙin Amurka

Ku dakatar da tarukan jam’iyya, ku dauki darasi daga Zamfara da Filato – INEC ta gargadi ADC

Ku dakatar da tarukan jam'iyya, ku dauki darasi daga Zamfara da Filato - INEC ta gargadi ADC Ku dakatar da tarukan jam'iyya, ku dauki darasi daga Zamfara da Filato - INEC ta gargadi ADC
Ku dakatar da tarukan jam'iyya, ku dauki darasi daga Zamfara da Filato - INEC ta gargadi ADC

Shugaban hukumar zaɓe ta kasa INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya bukaci jam’iyyar ADC da ta dakatar da shirinta na gudanar da babban taron ƙasa domin kauce wa matsalolin doka.

Ya ce wannan gargadi ya zama dole ne domin kada a maimaita irin kura-kuran da suka faru a jihohin Zamfara da Filato, inda rikice-rikicen cikin gida suka jawo matsala a harkokin zaɓe.

INEC ta bayyana cewa har yanzu akwai shari’a a kotu kan rikicin shugabanci a ADC, don haka duk wani mataki da ya saba wa umarnin kotu na iya haifar da matsala ga jam’iyyar.

Gargadin na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin cikin gida ke ci gaba da tsananta a ADC, gabanin zaɓen shekarar 2027.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use