Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Iran ta yi watsi da wa’adin sa’a 48 da Trump ya bayar

Jagoran addinin Iran Jagoran addinin Iran
Jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei (IRINN)

Iran ta yi watsi da wa’adin da sa’a 48 da shugaban Amurka Donald Trump ya sanya mata cewa a cimma yarjejeniya ko a buɗe mashigar Hormuz.

Wata sanarwa da shugaban rundunar ƙoli ta sojin Iran, Janar Ali Abdollahi ya fitar, ya kwatanta Trump a matsayin mutum mai wauta.

Ya yi gargaɗin cewa abin da Trump ke fatan saukar wa Iran zai kare kan Amurka.

“Idan Amurka ta kai hari kan muhimman kayayyakin more rayuwa na Iran, to Tehran za ta kai hari kan wuraren da sojojin Amurka da Isra’ila,” in ji shi.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use