Yayin da ake ci gaba da samun ƙaruwar ce-ce-ku-ce kan gyaran dokar zaɓe, musamman tanade-tanaden da suka shafi tura sakamakon zaɓen ta intanet wasu fitattun ‘yan Najeriya na kara shiga zanga-zangar neman a yi daidai.
Na baya-bayan nan daga cikin wadanda suka bi sahun masu zanga-zangar shi ne tsohon ministan sufurin kasar Rotimi Amaechi.
An hangi tsohon gwamnan Jihar ta Ribas kuma jigo a jam’iyyar ADC cikin masu zanga zangar da ke wakana a zauren shiga majalisar ta dokoki.
A cikin wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, an hangeshi tare da sauran masu zanga zanga yana karfafa musu guiwa.
Daga cikin masu zanga-zangar akwai gamayyar kungiyoyin fararen hula da na matasa da kuma masu rajin kishin dimokuradiyya da kuma jam’iyyun adawa.
Idan za’a iya tunawa dai, a jiya Litinin shima dan takarar shugaban kasa a tutar jam’iyyar Labour Party Peter Obi da ‘yar gwagwarmaya Aisha Yesufu sun bi sahun masu zanga-zangar.
Ko da yake shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya yi kiran zaman gaggawa a yau Talata don tattauna batutuwan da suka tayar da zanga-zangar.