Tawagogi daga Amurka da Iran na shirin isa Pakistan a ranar Juma’a domin gudanar da wata muhimmiyar tattaunawa, kamar yadda Firaministan Pakistan, Shehbaz Sharif, ya bayyana.
Sai dai rahotanni sun ce akwai rashin daidaito kan jerin mutanen da za su halarci wannan ganawa.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambaton wasu majiyoyi biyu daga Pakistan da ba a bayyana sunayensu ba, na cewa mataimakin shugaban Amurka, JD Vance, ne zai jagoranci tawagar Amurka, kuma zai gana da Kakakin Majalisar Dokokin Iran da kuma Ministan Harkokin Wajen Iran a birnin Islamabad.
A wani bangare kuma, shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana wa kafafen yada labaran kasar cewa tattaunawar kai-tsaye da Iran za ta gudana nan ba da jimawa ba.
Ya kuma yi nuni da cewa JD Vance na iya rashin halartar wannan ganawa saboda dalilai na tsaro.