Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Amurka ta bukaci gwamnatin Tinubu ta dauki mataki kan harin Filato

Trump na shirin daukar mataki mai hadari ga Amurka ko Iran Trump na shirin daukar mataki mai hadari ga Amurka ko Iran
Trump na shirin daukar mataki mai hadari ga Amurka ko Iran

Gwamnatin Amurka ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta yi Allah-wadai da hare-haren da suka faru a Jos, Jihar Filato, tana mai bayyana su a matsayin abin da ba za a amince da shi ba.

A cikin wata sanarwa, Amurka ta bukaci gwamnatin Bola Ahmed Tinubu da ta gaggauta ɗaukar matakai masu ƙarfi domin inganta tsaro da kare rayukan jama’a, musamman a wannan lokaci na bukukuwan addini.

Haka kuma, jami’an Amurka sun nuna damuwa kan yadda ake kai hare-hare kan fararen hula, tare da kira ga hukumomin Najeriya su ƙara ƙaimi wajen dakile tashin hankali da kuma gurfanar da masu hannu a hare-haren gaban kuliya.

Rahoton ya kuma nuna cewa wannan kira na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar ƙalubalen tsaro a wasu sassan ƙasar, inda hare-hare ke ƙara yawaita, musamman a yankunan Arewa da tsakiyar Najeriya.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use