Ofishin jakadancin Amurka a Beirut ya yi gargadi ga dukkan ‘yan Amurka da ke Lebanon su kaura daga yankin, sakamakon jerin hare-hare da Isra’ila take kaiwa a birnin, musamman kan rundunar Hezbollah.
Ofishin jakadancin ya kuma zargi yiwuwar rundunar IRGC ta Iran da kai hare-hare kan kadarorin Amurka a Beirut, yana mai cewa irin ayyukan Iran a kasashen makwabta na iya haifar da barazana ga tsaro a yankin.
An bayyana wannan lamari a matsayin babban sauyi ga tsare-tsaren tsaro a Lebanon da yankin baki ɗaya.