Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Amurka ta gargadi ‘yan ƙasarta a Najeriya da su yi taka tsantsan

Gwamnatin Amurka ta gargadi ‘yan ƙasarta da ke zama a Najeriya da sauran ƙasashe da su yi kaffa-kaffa saboda karuwar tashin hankali tsakanin Washington da Tehran.

Wannan na dauke ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar, inda ta yi kira ga ‘yan ƙasar su yi taka tsantsan musamman ma a wannan lokaci da kasar Amurkan da Isra’ila da Iran ke ci gaba da gwabza fada.

Sanarwar ta bayyana cewa hare-haren Amurkan da Isra’ila da kuma Iran ya shafi bangaren tafiye -tafiye da kuma kasuwanci a duniya.

Kazalika sanarwar ta shawarci ‘yan Amurka su yi rijista a shirin rijistar matafiya don samun sabbin bayanai na tsaro, tare da bibiyar shafuka da kasar Amurkan ta tanada don samun bayanai da suka kamata.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use