Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Ana cikin fargaba a yankin Gabas ta Tsakiya

Iran ta kai harin ramuwar gayya kan ƙadarorin Amurka a Gabas ta Tsakiya, ciki har da Bahrain, Kuwait, Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa, bayan harin hadin gwiwa na Amurka da Isra’ila.

Rundunar juyin-juya- halin Iran ta ce dukkan cibiyoyin soja na Amurka da Isra’ila a yankin an kai musu hare-haren ban mamaki da makamai masu linzami, kuma za a ci gaba da hare-haren har sai an kakkaɓe abokan gaba.

A Abu Dhabi, babban birnin Hadaddiyar Daular Larabawa, an ba da rahoton mutuwar akalla mutum ɗaya da kuma daƙile wasu makamai masu linzami da Iran ta jefa.

A Bahrain an kai hari kan hedkwatar rundunar ruwa ta “5th Fleet”, ko da yake ƙasar ta bayyana harin a matsayin “ta’addanci da take mata hakki.”

A halin da ake ciki dai, ƙasashen Qatar, Kuwait da Hadaddiyar Daular Larabawa sun rufe sararin samaniyarsu, yayin da Qatar ta ce ta dakile hare-hare kafin su shiga ƙasar.

Yanzu haka yankin na Gabas ta Tsakiya na cikin fargaba, yayin da tattaunawar zaman lafiya tsakanin Iran da Amurka a Oman da Geneva ta tsaya bayan harin na Amurka da Isra’ila a kan Iran.

Tuni dai ƙasar Saudiyya ta yi Allah-wadai cikin “kakkausar harshe” da harin da Iran ta kai kan ƙasashen na gabas ta tsakiya, inda ta yi gargadin ɗaukar mummunan martani muddin Iran ta ci gaba da hakan.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use