Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Gwamnan Zamfara ya bai wa limamai kyautar motoci 40

Gwamnan Zamfara Ya Bai wa Limamai Kyautar Motoci 40

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, a ranar Juma’a, ya bai wa Limamai 40 na masallatan Juma’a a fadin jihar motoci domin tallafa musu wajen gudanar da ayyukansu na addini yadda ya kamata.

Yayin da yake jawabi a wajen miƙa motocin, gwamnan ya ce an yi wannan tallafin ne domin inganta zirga-zirgar limaman, ta yadda za su ƙara faɗaɗa wa’azinsu da kuma hulɗa da al’umma.

Ya bayyana cewa Jihar Zamfara tana da tushe mai karfi a kan koyarwar addinin Musulunci, inda limamai ke yi wa al’umma hidima a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar. Ya ƙara da cewa jin daɗin shugabannin addini na daga cikin muhimman abubuwan da gwamnatinsa ta sa a gaba.

A cewarsa, limamai 40 da suka ci gajiyar motocin su ne rukunin farko na wannan shiri, wanda za a ci gaba da aiwatar da shi nan gaba.

“Muna kan gina masallatai da gidaje wa limamai, kuma muna ganin yana da muhimmanci su riƙa zirga-zirga cikin sauki,” in ji shi.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use