Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Gwamnonin Najeriya sun yi Alla-wadai da hare-haren kunar bakin wake a Maiduguri

Abdurahman Abdurazak, Gwamnan Kwara, Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya

Kungiyar Gwamnonin Najeriya, NGF, ta bayyana hare-haren kunar bakin-wake da aka kai a Maiduguri a daren Litinin a matsayin abin takaici da kuma kyama.

Kungiyar a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Talata ta hannun shugabanta, gwamna Abdulrahaman Abdulrazaq, ta ce abubuwan da suka faru sun kasance barnatar da rayukan mutane ba tare da wani dalili ba.

Kungiyar ta bukaci hukumomin tsaro da su dakile barazanar ‘yan ta’adda wajen kai irin wadannan hare-hare.

Ta kuma yi Alla-wadai da hare-haren da aka kai tare da tabbatar wa jami’an tsaro ci gaba da goyon bayan ayyukan da za su kawo karshen wannan matsala.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use