Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Hukumar DSS ta kame wanda ya kitsa harin Cocin ECWA a shekarar 2025

Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun kama wani mai suna Shafi’u Usman, wanda ake zargi da hannu a harin da aka kai Cocin ECWA dake Ayetoro, a Jihar Kogi.

Rahotanni sun bayyana cewa, an kai harin ne lokacin da masu ibada ke tsaka da ibada a Cocin ranar 14 ga watan Disamba 2025. Hukumar tayi nasarar cafke Shafi’u Usman ne a maboyar sa dake jihar Gombe.

Yayin da yake amsa tambayoyi, Shafi’u Usman, ya amsa aikata laifin da ake tuhumarsa inda ya bada tabbacin da hannun sa a harin na cocin tare da amsa wasu zarge zarge na garkuwa da mutane a jihohin Niger, Kwara da Kogi.

Kazalika ya bayyana sunan wani Ibrahim Dattijo a matsayin wanda ke bashi gudummawa wajen ta’addanci a jihohin Niger, Kwara, Kogi dama Jihar Zamfara, kuma ya bayyana shi a matsayin mai sayar masa da makamai da harsasai.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use