Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Iran na ci gaba da ruwan wuta kan Isra’ila

Lokuta kadan bayan nada sabon shugaban addini an Iran Mojtaba Ali Khamene’i, Iran ta sake kai zafafan hare-hare kasar Isra’ila.

Rahotanni daga kafar yada labarai ta AFP ta ce Iran ta sake kai hare-hare sassan Isra’ila ta hanyar amfani da makamai masu linzami waɗanda a wannan karon ta yi ruwansu lokaci guda a yankunan kudanci da arewacin ƙasar.

Kafin yanzu Iran din na kai hare-hare ne daban-daban a sassan Isra’ila, sai dai ruwan makaman da Iran din ta yi a yau Litinin ya sha bambam, gabar da aka shiga mako na biyu da fara yaƙin ƙasashen.

Kazalika rahoton ya kara da cewa, an ji ƙarar na’urar ankararwa a birane da dama na Isra’ilar tun daga Haifa har zuwa Dimona.

Iran ta yi wa kasar Isra’ila gagarumar barna a hare-haren da ta ke kai wa, sai dai Isra’ila ta yi nasarar kakkabe wasu daga cikin makamai masu linzami da Iran din ta harba.

Rahotanni sun ce hare-haren sun shafi yankunan Tel Arad da Dimona waɗanda ke gaba da Negev, wato yankin da cibiyar binciken makaman nukiliya na ƙasar yake.

Haka-zalika an ji kuwwar ankararwa a Tiberias da tsaunukan Jezreel, Beisan da kuma kwarin Galilee.

Ko da yake Isra’ila ta fitar da sanarwar cewa ta sanya kuwwar ne don ankarar da jama’arta, amma ba don hare-haren da Iran take mata suna tasiri ba.

Mazauna yankunan da Iran ta harba makaman dai sun ce sun ji ƙarar fashe-fashe, sai dai sun ce ba su da tabbacin ko ƙarar na’urorin da ke tare makamin da Iran ke aika wa ne ko kuma na saukar makaman ne.

A jiya ne dai kasar Iran ta amince da nadin Mojtaba Ali Khmanei, da ga marigayi Ali Khamenei wanda ya rasu a harin farko da Isra’ila ta kai a makon farko da fara yakin.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use