Alireza Bikdeli, jakadan Iran a Afghanistan, ya nuna godiya ga shugabannin Taliban sakamakon matakin da suka ɗauka na ƙin miƙa sansanin sojin saman Bagram ga Amurka, yana mai cewa Musulunci yana kare kowa.
Da yake magana da Shamshad TV, ya ce kasancewar sansanin sojin Amurka a can zai iya haifar da rikici tsakanin Iran da Afghanistan.
Bikdeli ya kara da cewa kin amincewar Taliban ya dogara ne kan imani na addini da kuma ka’idar Musulunci cewa kada musulmai su taimaki wadanda ba musulmi ba su kai hari ga wasu musulmai.
A shekarar 2025, an ruwaito cewa gwamnatin Donald Trump ta tattauna da Taliban kan mika sansanin sojin saman Bagram don musayar taimakon kudi da kuma dage takunkumi, amma Kabul ta yi watsi da tayin.