Kotun daukaka kara ta tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya dakatar da taron ƙasa na jam’iyyar PDP.
A ranar Litinin, kotun ta yi watsi da ƙarar da wani ɓangare na jam’iyyar karkashin jagorancin Taminu Turaki ya shigar.
Kwamitin gudanarwar jam’iyyar na ƙasa bangaren Turaki, wanda ke ikirarin cewa shi ne halastaccen shugaban jam’iyyar ta adawa, an ce an zaɓe shi ne a taron jam’iyyar da aka yi a Ibadan.
Kotun ta kuma umarci Turaki da sauran mambobin gudanarwa da suka shigar da ƙarar su biya tarar naira miliyan 2 saboda ƙarar da suka kai.
Rahotanni sun nuna cewa Kotun Ƙorafi da ke Abuja ta sanya ranar Litinin domin yanke hukunci kan ƙorafe-ƙorafe da aka haɗa wuri guda, waɗanda suka samo asali daga taron ƙasa na jam’iyyar PDP da aka yi a Ibadan ranar 15 zuwa 16 ga Nuwamba, 2022.