Ma’aikatar Lafiya ta Isra’ila ta ce aƙalla mutum 1,929 ne aka kwantar a asibiti tun bayan barkewar yaƙi da Iran, ciki har da 157 a cikin awanni 24 da suka gabata.
Ma’aikatar ta ce daga cikin waɗanda aka kwantar, mutum tara na cikin mawuyacin hali, yayin da 42 suka samu matsaƙaitan raunuka, sannan 70 kuma suka ji ƙananan raunuka.
Ta yi bayanin cewa mutane da dama sun ji rauni ne yayin da suke sauka zuwa wuraren mafaka, domin kare kansu daga hare-haren makamai.