Madugun ɗarikar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya sanar da komawa jamʼiyyar ADC tare da ɗimbin magoya bayansa a hukumance.
Kwankwaso ya bayyana haka ne yayin wani taro da aka gudanar a gidansa da ke Kano.
Tsohon gwamnan na Kano ya kuma buƙaci mabiyansa da su yi rajista da jam’iyyar ta ADC, domin shirya fafatawa a zaɓukan ƙasar da ke tafe.
A ranar Lahadi, Kwankwaso ya sanar da ficewa daga jam’iyyar NNPP, inda ya ce ya zama tilas a sama wa ‘yan Najeriya mafita.