Rundunar sojin Najeriya ta kai wani gagarumin farmaki kan maboyar fitaccen shugaban ƴan bindiga, Bello Turji, inda aka hallaka ƴan bindiga da dama bayan wani artabu mai zafi.
Rahotanni sun bayyana cewa sojojin sun kai harin ne a wuraren da ake zargin ƴan bindigar na ɓoye, inda suka yi amfani da ƙwarewar dabarun yaki da kuma ƙarin ƙarfi domin murƙushe su.
A yayin farmakin, an yi musayar wuta mai zafi tsakanin ɓangarorin biyu, lamarin da ya kai ga fatattakar ƴan bindigar daga maboyarsu.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa sojojin sun samu nasarar kashe da dama daga cikin ƴan bindigar, yayin da wasu suka tsere da raunuka.
Bello Turji na daga cikin fitattun shugabannin ƴan bindiga a arewa maso yammacin Najeriya, musamman a jihohin Zamfara da Sokoto, kuma ana danganta shi da hare-hare da dama da suka yi sanadiyyar asarar rayuka da dukiyoyi.