Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske
Azumi 30 za a yi bana in ji masana
Tinubu ya bai wa mukarrabansa masu son tsayawa takara wa’adin mako biyu su yi murabus
Sojojin Najeriya sun hallaka ƴan ta’adda 61 a jihar Borno

Tinubu ya bai wa mukarrabansa masu son tsayawa takara wa’adin mako biyu su yi murabus

Tinubu Tinubu
Shugaban Najeriya Bola Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya umarci masu mukamai da aka nada a gwamnatinsa da ke sha’awar tsayawa takara a zaben 2027, cewa su ajiye aiki nan da makonni biyu.

Sanarwar da ta fito daga ofishin sakataren gwamnatin ta bayyana cewa masu son tsayawa takarar za su fara murabus daga yau har zuwa ranar 31 ga watan Maris.

Shugaba Tinubu yace, wannan mataki ya zama dole, saboda a tabbatar an bi duk wata ka’ida da hukumar zabe ta fitar, don samun sahihin sakamako a zabukan 2027 dake tafe.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use