Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Tinubu ya nemi a gyara kundin tsarin mulkin Najeriya don samar da ‘Yan sandan jihohi

Shugaban Nageriya Bola Ahmed Tinubu ya roki Majalisar Dattawa da ta sauya kundin tsarin mulki domin ba da damar kafa ‘yan sandan jihohi.

Ya bayyana bukatar a wani taron buda-baki da ya yi tare da sanatoci a fadar shugaban ƙasa a ranar Laraba.

Tinubu ya ce ‘yan sanda na jiha suna da muhimmanci wajen magance matsalolin tsaro, inganta aikin ‘yan sanda a matakin ƙasa, da ba jihohi damar mayar da martani cikin sauri ga barazanar tsaro.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use