Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Yansanda sun fara binciken gawar da aka tsinta a wani tsauni a Adamawa

Yansanda Yansanda
Ana ci gaba da bincike don gano musabbabin mutuwar (Getty Images)

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta tabbatar da samun rahoton tsintar gawar wani mutum rataye a jikin bishiya a ƙasan Dutsen Bagale na ƙaramar hukumar Girei.

Tuni aka garzaya da gawar zuwa asibiti, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.

Wani rahoton da ba na ‘yan sanda ba ya bayyana cewa marigayin mai suna Ahmed Mohammed mai shekara 46 shi ya kashe kansa ta hanyar rataya.

Ana ci gaba da bincike domin gano musabbabin mutuwar mutumin a yanzu.

Rundunar ‘yansandan ta yi kira ga al’umma da duk wanda ke da wata muhimmiyar shaida da za ta taimaka wajen binciken da su fito su taimaka wa ‘yansanda.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use