Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya isa babbar kotun Jihar Kaduna domin ci gaba da shari’arsa da Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ke yi.
Idan ba’amanta ba kotun ta ɗage sauraron buƙatar beli da ya gabatar zuwa ranar 14 ga Afrilu.
ICPC ta gurfanar da El-Rufai a gaban kotu kan tuhume-tuhume guda 10, waɗanda suka haɗa da zargin karkatar da kadarorin gwamnati da kuma wanke kuɗaɗe.