Kotun Koli ta jinkirta yanke hukunci kan rikicin shugabancin jam’iyyar hamayya ta ADC, wanda ta fara saurara a yau Talata gabanin zaben 2027.
A ranar Laraba ne kotun kolin ta fara sauraron karar da aka shigar gaban ta kan takaddamar shugabanci a jam’iyyar ADC.
Alkalai biyar ne ke sauraron karar.
A gefe guda kuma, kotun ta saurari karar da ta shafi rikicin shugabanci a jam’iyyar PDP da makamantansu.
Dukkan shari’o’in biyu dai na nuni da irin rigingimun cikin gida da ke gudana a tsakanin manyan jam’iyyun adawar Najeriya gabanin zaben 2027.
Wani bangare karkashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark ne ya shigar da karar ADC, wanda ke fafutukar neman takarar shugabancin jam’iyyar.
Rikicin ya kuma shafi tsohon minista Rauf Aregbesola da wasu ‘ya’yan jam’iyyar.
Mark yana kalubalantar hukuncin da wata karamar kotu ta yanke wanda ya ba da damar gudanar da shari’a kan takaddamar shugabancin.
Ya ce bai kamata kotuna su yanke hukunci kan al’amuran cikin gida ba. Tawagar lauyoyinsa ta bukaci kotun kolin da ta yi watsi da karar da bangaren Nafiu Bala Gombe tare da neman ta mayar da ikon a bangarensa don ci gaba da gudanar da al’amuran jam’iyyar.