Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Cin amana da yaudara na hana ci gaban Najeriya – Dr Gadon Kaya

Cin amana da yaudara na hana ci gaban Najeriya - Dr Gadon Kaya Cin amana da yaudara na hana ci gaban Najeriya - Dr Gadon Kaya
Cin amana da yaudara na hana ci gaban Najeriya - Dr Gadon Kaya

Limamin masallacin Usman bn Affan a Gwale, Jihar Kano, Dr. Abdullah Usman Gadon Kaya, ya ce yawaitar cin amana da yaudara na daga cikin abubuwan da ke hana ‘yan Najeriya jin daɗin rayuwa da samun ci gaba.

Ya bayyana hakan ne a hudubar Juma’a, inda ya ce waɗannan halaye sun zama ruwan dare, suna haifar da matsaloli a rayuwar yau da kullum, ciki har da tauye ma’auni da ƙarya domin neman abin duniya.

Malamin ya kuma zargi wasu shugabanni da rashin kishin al’umma, tare da gargadin cewa neman mulki da kuɗi ta kowace hanya har da caca na ƙara lalata zamantakewa.

Ya buƙaci jama’a da su rungumi gaskiya da riƙon amana domin gyaran al’umma.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use