Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

NDA ta gargadi jama’a kan ƴan damfara a Intanet

NDA ta gargadi jama’a kan ƴan damfara a Intanet NDA ta gargadi jama’a kan ƴan damfara a Intanet
NDA ta gargadi jama’a kan ƴan damfara a Intanet

Makarantar horar da sojoji ta NDA ta yi gargadi ga jama’a kan wasu ‘yan damfara da ke amfani da sunan kwamandanta wajen aikata zamba ta yanar gizo.

Hukumar ta bayyana cewa ana ƙirƙirar asusun bogi a kafafen sada zumunta domin yaudarar mutane da tayin ƙarya kamar kwangiloli da sauran damammaki.

Ta jaddada cewa ba ta da alaƙa da irin waɗannan saƙonni, tare da buƙatar jama’a su rika tantance sahihancin bayanai kafin su amince da su.

NDA ta kuma gargaɗi cewa duk wanda aka kama da hannu a irin wannan damfara zai fuskanci hukunci mai tsanani bisa doka.

A ƙarshe, ta buƙaci jama’a su yi hattara tare da kai rahoton duk wani abu mai kama da zamba ga hukumomin da suka dace.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use