Tsohon gwamnan Sokoto, Aminu Tambuwal, ya zargi gwamnatin Bola Tinubu da shirin raunana jam’iyyun adawa kafin zaɓen 2027.
Ya bayyana hakan ne bayan taron ADC a Sokoto, yana mai cewa yanayin siyasa na nuna barazana ga dimokuraɗiyya.
Tambuwal ya ce ana ƙoƙarin tabbatar da cewa babu wata jam’iyya da za ta zauna lafiya sai APC.
Ya kuma nuna cewa rikice-rikicen da ke faruwa a jam’iyyar Labour Nigeria da PDP na iya zama sakamakon matsin lamba.
A ƙarshe, ya ce sauya sheƙar gwamnoni zuwa APC na faruwa ne saboda tsoro da neman tsira a siyasa, ba don aiki ba.