Wasu ‘yan Najeriya sun soki gwamnati kan yawaitar tafiya ƙasashen waje domin neman magani, suna mai cewa hakan na jawo asarar makudan kuɗaɗe tare da nuna raunin tsarin kiwon lafiya na cikin gida.
Rahotanni sun nuna cewa ƙasar na rasa biliyoyin daloli a kowace shekara sakamakon “zuwa kasashen waje jinya”, inda masu hali da wasu jami’an gwamnati ke fifita jinya a waje maimakon asibitocin gida.
Masana sun ce wannan na raunana tattalin arziki, tare da ƙara matsin lamba ga darajar naira, sakamakon fitar kuɗaɗe zuwa ƙasashen waje.
An danganta matsalar da ƙarancin kayan aiki, rashin ƙwararru, da kuma rashin amincewar jama’a da asibitocin cikin gida.
Sai dai masana sun jaddada cewa ƙarin zuba jari da inganta harkar lafiya zai taimaka rage asarar da ƙarfafa tsarin kiwon lafiya na ƙasa.