Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske
Zeenatu Zakzaky ta bukaci shugabannin addinai su nisanci rashin adalci
2027: Magoya bayan Obi da Kwankwaso sun kaddamar da OK Movement domin karfafa hadin kan ‘yan adawa a Najeriya
Kotun koli ta dage shari’ar masarautar Kano zuwa Afrilu 2027

2027: Magoya bayan Obi da Kwankwaso sun kaddamar da OK Movement domin karfafa hadin kan ‘yan adawa a Najeriya

2027: Magoya bayan Obi da Kwankwaso sun kaddamar da OK Movement domin karfafa hadin kan ‘yan adawa a Najeriya 2027: Magoya bayan Obi da Kwankwaso sun kaddamar da OK Movement domin karfafa hadin kan ‘yan adawa a Najeriya
2027: Magoya bayan Obi da Kwankwaso sun kaddamar da OK Movement domin karfafa hadin kan ‘yan adawa a Najeriya

Magoya bayan tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi, da na tsohon gwamnan Kano, Rabiu Kwankwaso, sun kaddamar da sabuwar tafiya mai suna Obi–Kwankwaso (OK) Movement domin ƙarfafa haɗin kan ‘yan adawa gabanin zaɓen 2027.

An bayyana ƙaddamar da tafiyar ne a Abuja, inda aka ce an riga an fara shimfiɗa tsare-tsare a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya, tare da naɗa wakilai a matakan jiha da shiyya don gudanar da ayyukan wayar da kai.

Sakataren yaɗa labaran ƙungiyar, Justin Ijeh, ya ce haɗakar ta haɗa mambobi daga Obidient Movement, Kwankwasiyya Movement, NNPP da kuma African Democratic Congress (ADC), domin ƙarfafa hadin gwiwar siyasa.

Ya bayyana cewa matsalolin tattalin arziki, tsadar rayuwa da rashin tsaro ne suka sa aka kafa wannan dandali, wanda ke da nufin samar da sabon salo a siyasar Najeriya.

A cewarsa, OK Movement na da burin zama wata kafa ta haɗin kai da za ta ba da gudunmawa wajen gina sabuwar makomar siyasa a ƙasar gabanin babban zaɓen 2027.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use