A yayin da ake shirin gudanar da tattaunawa kai tsaye tsakanin Isra’ila da Lebanon a birnin Washington, DC ranar Talata, rahotanni sun nuna cewa Isra’ila ta rage ayyukan sojojinta na sama a Lebanon sakamakon matsin lamba daga Amurka.
Wata kafar yaɗa labarai ta Isra’ila, Channel 13, ta ruwaito cewa an takaita ayyukan ne zuwa tallafa wa sojojin ƙasa da kuma dakile hare-haren da ƙungiyar Hezbollah ke kai wa Isra’ila.
Rahoton ya ƙara da cewa an dakatar da hare-haren sama a birnin Beirut da kuma wasu yankuna masu zurfi a cikin Lebanon, a wani mataki na rage tashin hankali gabanin fara tattaunawar.