Wata kotu a babban birnin tarayyar Najeriya Abuja, ta bai wa hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC, izinin kama tsohuwar ministar jin-ƙai ta ƙasar Sadiya Umar Faruoq.
EFCC dai na binciken tsohuwar ministar da badaƙalar dala miliyan $1.3m da kuma Naira miliyan N746.6m na ma’aikatar da ake zargin an yi sama da fadi da shi.
Wani saƙo da EFCCn ta wallafa a shafinta na X, ta ce mai shari’a Jude Onwuegbuzie, ya kuma ba da izinin kama sakataren ma’aikatar Bashir Nura Alkali.
Hukumar ta ce matakin ya zo bayan ƙin bayyana a gaban kotu da waɗanda ake zargin suka yi a ranar Alhamis.
Lauyan waɗanda ake ƙarar sun buƙaci a ba su uzuri sakamakon rashin lafiya da ya hana Sadiya Farouq halartar kotun, sai dai kotun ba ta amince da buƙatar tasu ba.