An kashe Ministan Tsaron ƙasar Mali, Janar Sadio Camara, yayin wasu hare-hare da ‘yan bindiga suka kai kan sansanonin soji a sassa daban-daban na ƙasar, kamar yadda wasu majiyoyi suka shaida wa Al Jazeera.
Rahoton da ya fito a ranar Lahadi ya zo ne kwana guda bayan an kai hari gidansa da ke sansanin soji na garin Kati.
Camara ya kasance jigo a gwamnatin sojin da ta karɓi iko da Mali bayan juyin mulki biyu da suka faru a shekarun 2020 da 2021.

Masana tsaro da siyasa na cewa mutuwarsa babbar illa ce ga rundunar sojin ƙasar wacce ke yaki da ‘yan bindiga.
Maharan sun kai hari ne ta amfani da motar kunar bakin wake a gidan Camara da ke Kati, wani gari mai tsauraran matakan tsaro na soji da ke kimanin kilomita 15 a Arewa maso yammacin babban birnin ƙasar, Bamako.