Gwamnatin jihar Cross River ta karyata rahotannin cewa an samu karin mutane 10 da ke nuna alamun COVID-19.
Ta ce rahoton ba gaskiya ba ne kuma yana iya haifar da rudani.
Gwamnatin ta jaddada cewa mutum guda ne kawai aka tabbatar ya kamu da cutar a jihar.
Wannan martani ya biyo bayan wani rahoto da ya tayar da hankula, inda aka ce an gano sabbin mutum 10 da suka kamu da cutar a wasu yankunan jihar.
Kwamishinan lafiya a jihar, Dakta Henry Ayuk, ya bayyana cewa wanda aka tabbatar da cutar ɗan ƙasar China ne da ke aiki a jihar, kuma yana samun kulawa da magani cikin nasara.
Ya ce mutum 10 da aka ambata a rahoton su ne kawai wadanda suka yi mu’amala da wanda ya kamu, kuma ba su nuna alamun cutar ba.
A cewarsa, an killace su ne a matsayin matakin kariya, ba wai don sun kamu da cutar ba ne.