Yanayin Duhu Yanayin Haske
Yanayin Duhu Yanayin Haske

Gwamnatin Cross River ta musanta cewa sabbin mutum 10 sun kamu da COVID-19

Gwamnatin Cross River ta musanta cewa sabbin mutum 10 sun kamu da COVID-19 Gwamnatin Cross River ta musanta cewa sabbin mutum 10 sun kamu da COVID-19
Gwamnatin Cross River ta musanta cewa sabbin mutum 10 sun kamu da COVID-19

Gwamnatin jihar Cross River ta karyata rahotannin cewa an samu karin mutane 10 da ke nuna alamun COVID-19.

Ta ce rahoton ba gaskiya ba ne kuma yana iya haifar da rudani.

Gwamnatin ta jaddada cewa mutum guda ne kawai aka tabbatar ya kamu da cutar a jihar.

Wannan martani ya biyo bayan wani rahoto da ya tayar da hankula, inda aka ce an gano sabbin mutum 10 da suka kamu da cutar a wasu yankunan jihar.

Kwamishinan lafiya a jihar, Dakta Henry Ayuk, ya bayyana cewa wanda aka tabbatar da cutar ɗan ƙasar China ne da ke aiki a jihar, kuma yana samun kulawa da magani cikin nasara.

Ya ce mutum 10 da aka ambata a rahoton su ne kawai wadanda suka yi mu’amala da wanda ya kamu, kuma ba su nuna alamun cutar ba.

A cewarsa, an killace su ne a matsayin matakin kariya, ba wai don sun kamu da cutar ba ne.

Samu labarai ta Email

Idan kuka danna maballin subscribe, kuna tabbatar da cewa kun karanta kuma kun yarda da mu. Privacy Policy and Terms of Use