Ƙungiyar Tarayyar Turai na shirin faɗaɗa takunkuminta kan Iran domin haɗa duk waɗanda ake zargi da hana zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar Hormuz.
Jami’an diflomasiyya sun bayyana cewa an cimma matsaya don hukunta mutane da kamfanonin da ke da hannu wajen toshe wannan muhimmiyar hanya ta ruwa.
Wannan mataki na zuwa ne bayan Iran ta rufe mashigar sakamakon rikicin yaƙi, lamarin da ya shafi kusan kashi ɗaya bisa biyar na man fetur da iskar gas na duniya.
Ana sa ran ƙarin sunayen waɗanda za a kakabawa takunkumi cikin makonni masu zuwa, yayin da rikicin ke ci gaba da tayar da hankalin duniya.