Shugaban ƙasar France, Emmanuel Macron, ya yi kira ga Amurka da Iran da su rage zafin rikici da ke ƙara ƙamari a yankin mashigar Strait of Hormuz.
Macron ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da ya gudanar tare da Firayim Ministan Poland, Donald Tusk, inda ya jaddada cewa hanyar diflomasiyya ce kaɗai mafita mai dorewa ga rikicin.
Ya ce matsayar ƙasarsa ba ta canza ba, yana mai cewa dole ne a warware matsalolin ta hanyar tattaunawa da fahimtar juna, tare da kira ga dukkan ɓangarorin da su kwantar da hankulansu.
Haka kuma, Macron ya tabbatar da cewa ba a kai hari kai tsaye ga Faransa ba, duk da harbe-harben gargadi da Iran ta yi a ranar Asabar kan wasu jiragen ruwa da ke wucewa ta mashigar.
Daga cikin jiragen da abin ya shafa har da na kamfanin CMA CGM, inda kamfanin ya bayyana cewa harbe-harben gargadi ne kawai, kuma babu wani lahani da ya samu ga ma’aikatan jirgin.